Connect with us

News

’Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 3, Sun Sace Wasu 16 A Kauyukan Kaduna

Published

on

 

 

 

Kasa da awa 24 bayan ’yan bindiga sun sace wani jaririn da wata mai jego ta haifa a sansaninsu, an sake kashe mutum uku tare da sace wasu 16 a kauyuka uku na Karamar Hukumar Kagarkon Jihar Kaduna.

 

Wani mazaunin yankin, Shehu Rabi’u, wanda ya tabbatar wada daily trust a faruwar harin ta wayar salula ranar Laraba, ya kuma ce an kai hare-haren ne a kauyukan Kala da Kutar da kuma Taka-Lafiya.

Advertisement

 

FIFA ta karbe daukar nauyin gasar kofin duniya daga Indonesia

Ya ce maharan, wadanda ke kan babura dauke da bindigu kirar AK-47, da farko sun kai hari ne kan wani matsugunin makiyaya da ke Taka-Lafiya, inda suka sace mutum shida, sannan suka kashe wani mai suna Malam Ya’u.

 

Ya ce daga nan ne maharan suka wuce kauyen Kutar mai makwabtaka da shi, inda a can ma suka yi awon gaba da mutum bakwai.

 

 

Advertisement

Kazalika, Shehu ya ce ’yan bindigar sun kuma karasa kauyen Kala suka sace mutum biyar bayan sun yi ta harbe-harbe.

 

“A lokacin da suke ta harbe-harben ne mutum biyu suka mutu a Taka-Lafiya, daya kuma a Kutar,” in ji Shehu.

 

Shi ma Madakin Janjala, wani kauye da ke da makwabtaka da inda aka kai hare-haren, Sama’ila Babangida, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce yana kan hanyarsa ta zuwa Jere lokacin da ya samu labarin.

 

Advertisement

 

Aminiya ta gano cewa ’yan bindigar dai na da sansanoninsu a Tagwayen Dutse, wani dajin gwamnati da ke tsakanin Kananan Hukumomin Kagarko da Kachia na jihar Kaduna.

 

 

Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoton babu wani karin bayani kan batun daga Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kadunan.

 

Advertisement

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending