News
Gwamna Ganduje Ya Rushe Majalisar Zartaswa Mako Ɗaya Gabanin Mika Mulki
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Kano mai barin gado, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya sallami baki ɗaya mambobin majalisar zartarwa daga bakin aiki.
Ganduje ya rushe majalisar zartaswansa a wani ɓangare na shirye-shiryen miƙa mulki ga zababben gwamna ranar 29 ga watan Mayu, 2023.
Babbar Sakatariya a ofishin Sakataren gwamnatin jihar Kano, Bilkisu Maimota, ce ta bayyana haka a wata sanarwa a ranar Litinin.
Sanarwar ta ce “Yayin da wa’adin zango na biyu na mulkin Gwamna Abdullahi Ganduje zai cika ranar 29 ga watan Mayu, 2023, ya zama wajibi jami’an gwamnati da ke riƙe da kujerun siyasa su sauka daga mukamansu.”
“Bisa haka ne, a hukumance muke umartan masu rike da naɗe-naɗen siyasa kama daga Kwamishinoni, mashawarta da sauran hadimai na musamman, mambobin gudanarwan hukumomi su miƙa ragamar ofisoshinsu.”
“Dukkan waɗanda abun ya shafa ana umartar da su miƙa ragama da duk wata kadarar gwamnati hannun Manyan Sakatarori ko Daraktoci daga nan zuwa ranar Jumu’a 26 ga watan Mayu.”
“Bugu da ƙari, Bilkisu Maimota, ta ce wannan umarnin bai shafi masu rike da muƙaman da wa’adinsu bai ƙare ba kamar yadda kundin dokoki hukumomin su suka ya tanada.
Ta bayyana cewa Gwamna Ganduje ya gode tare da jinjinawa jami’an gwamnatin bisa gudummuwar da suka bayar iya karfinsu wajen kawo ci gaba ga jahar Kano.”
Mai girma Gwamna ya na musu fatan Alheri a dukkan harkokin rayuwar da zasu sa gaba, inji Maimota.
Wa’adin Gwamna Ganduje zai ƙare a Litinin mai zuwa wato 29 ga watan Mayu, inda za a rantsar da Injiniya Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin sabon gwamnan jihar Kano.
