News
Kwalara ta ɓarke a ƙasashen Afirka 15 – WHO
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar lafiya ta duniya, WHO ta ce cutar kwalara ta barke a kasashen Afirka guda 15 ciki har da Afirka ta Kudu.A ciki akwai kuma Jamhuriyar Dumukuradiyyar Kongo (DRC) da Eswatini da Mozambique da Kenya da kuma Zimbabwe.
Shugaban kasa muhammad buhari zai ƙaddamar da Titin Kano zuwa Abuja a yau talata
Hukumar ta bayyana hakan ne bayan da mutum 15 ciki har da karamin yaro dan shekara uku suka mutu a Afirka ta Kudu a sanadiiyar kamuwa da cutar wadda ta fara mako daya da ya wuce.Akwai kuma wasu mutanen sama da 30 da ke kwance a asibiti a cikin mawuyacin hali a kasar ta Afirka ta Kudu.Hukumar ta WHO ta kuma ce Malawi ce ta fi yawan mutanen da suka kamu da cutar.Su kuwa hukumomin Afirak ta Kudu sun ce an dauki tsauraran matakai a iyakokin shiga kasar domin hana masu dauke da cutar shiga.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
