Connect with us

News

NiMet ta yi hasashen samun rana da tsawa daga ranar Litinin zuwa Talata a fadin kasar.

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Hukumar kula da yanayi ta kasa NiMet, ta yi hasashen samun rana da tsawa daga ranar Litinin zuwa Talata a fadin kasar.

Hasashen hukumar ta NiMet, wanda aka saki ranar Lahadi a Abuja, ya nuna cewa daga ranar Litinin rana da tsawa yankin arewacin kasar tare da yiwuwar tsawa da safe a sassan jihohin Adamawa, Taraba, Kaduna, Katsina, Zamfara, Kebbi da Sokoto.

Jami’ar Jihar Osun ta dakatar da wata daliba da ake zargin tana da hannu a fashin  da makami 

Haka kuma akwai yiwuwar yin tsawa a sassan jihohin Jigawa, Katsina, Kano, Kaduna, Bauchi, Gombe, Taraba da Adamawa.
“Ana sa ran samun iska mai tsananin yankin Arewa ta tsakiya tare da tsawa a sassan Kwara, Neja, Babban Birnin Tarayya Abuja, Jihohin Nasarawa da Binuwai.
Ana sa ran samun gajimare a kan jihohin Kudu da na gabar teku da ake sa ran za a samu ruwan sama mai matsakaicin karfi zuwa sassan jihohin Ogun, Oyo, Edo, Imo, Anambra, Ebonyi, Lagos, Bayelsa, Delta, Cross River, Rivers da Akwa Ibom.

NAN

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending