News
An ceto yara 7 a gidan marayu da ya kamata da wuta a Legas
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar Kwana-kwana ta jihar Legas (LASEMA) ta ce ta ceto wasu yara bakwai a wata gobara a gidan marayu a jihar Legas.
Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da Nosa Okunbor, shugaban sashen hulɗa da jama’a na LASEMA ya sanya wa hannu a yau Litinin da safe.
Rundunar Yan Sanda Sun Kama Wani Mutum Bisa Zargin Sayar Da ‘Ya’Yansa Uku
Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa LASEMA ta ce wutar ta tashi ne a cikin gidan daga na’urar sanyaya daki, bayan da aka kawo wuta mai ƙarfi a jiya Lahadi.
Sai dai kuma hukumar ta ce an ceto yara maza bakwai daga ginin mai hawa ɗaya da ke lamba 7 Wole Madariola St., kusa da Enitan Kusimo Street, Aguda, Lagos.
Advertisements
