News
DA DUMI-DUMI: Kotun Koli ta tabbatar da hukuncin daurin shekaru biyar kan Farouk Lawan
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotun koli ta tabbatar da hukuncin shekaru biyar da aka yankewa tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, bisa samunsa da laifin karbar cin hancin $500,000 daga hannun dan kasuwa Femi Otedola.
Rahotanni na nuni da cewa an dai yi shari’ar Lawan ne da laifin karbar cin hancin dala 500,000 a lokacin wani bincike da ‘yan majalisa suka yi kan tsarin tallafin man fetur a shekarar 2012.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jigawa, ta kama wasu mutum uku kan zargin satar awaki 48
Lauyan Lawan ya bukaci a soke hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke ranar 24 ga Fabrairu, 2022, inda ta yanke masa hukuncin daurin shekaru biyar a gidan yari tare da sallame shi a kan tuhume-tuhume biyu daga cikin ukun da ake tuhumarsa da laifin cin hanci da rashawa da gwamnatin tarayya ta yi masa. Gwamnati.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
