Connect with us

News

SHUGABAN KASA BOLA TINUBU YA KALLI RANTSUWAR DA USMAN ODODO DAGA KASAR FARIS

Published

on

Bola Ahmad tinubu shugaban kasar Nigeria

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Usman Ododo ya sha rantsuwar kama aiki a matsayin sabon gwamnan jihar Kogi da ke tsakiyar Najeriya, bayan nasarar lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar cikin watan Nuwamba.

An gudanar da bikin rantsuwar ne a Lokoja babban birnin jihar  a yau Asabar da rana, inda aka rantsar da shi tare da mataimakinsa, Salifu Joel Oyibo

Sabida mahimmancin rantsuwar yasanya shugaban kasa Bola tinubu ya kalli bidiyon  rantsuwar da Usman ododo daga   faris babban burnin faransa

Mista Ododo wanda ɗan jam’iyyar APC ne zai maye gurbin Yahaya Bello wanda ke kammala wa’adin mulkinsa na biyu. A Jigar kogin

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima, da gwamnan jihar Yahaya Bello da wasu jiga-jigan jam’iyyar APC, na daga cikin mutanen da suka halarci bikin rantsuwar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending