Connect with us

News

Dole ne mu bi kadin abinda aka yi wa Jami’anmu —Hukumar KAROTA 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Hukumar Kula da Zirga zirgar Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta kama daya daga cikin wadanda ake zargi da farwa Jami’anta

Hukumar ta sami nasarar kama matashin mai suna Saifullahi Haruna jim kadan bayan da wasu ɓata gari sun farwa Jami’an hukumar wadanda suke bincike ababen hawa a kan titin Panshekara cikin burnin Kano

AFCON 2023: Karon-battar da za mu yi da Najeriya za ta yi zafi sosai, amma daidai muke da Super Eagles – Kociyan Afrika ta Kudu

Hakan na kunshe ne ta cikin wata Sanarwa da  jami in yada labarin na Hukumar Nabilusi Abubakar K/Na’isa ya turawa da Jaridar Inda Ranka

Sanarwar ta kara da cewa wasu ɓata garin matasa ne suka farwa Jami’an na KAROTA da misalin karfe 3 na dare a kan titin Panshekara cikin burnin Kano.

Advertisement

Hukumar ta ce ba za ta zuba ido ta kyale ana cin zarafin Jami’anta ba, domin kuwa aiki suke bisa tsarin doka

Tuni dai Hukumar ta miķa wanda ta kama wajen Baturen Yans. andan yankin da abin ya faru domin fadada bincike tare da daukar matakin kama ragowar domin gurfanar da su gaban sharia

Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ya ce ya zama wajibi Hukumar ta mika godiyarta ga al’umma musamman wadanda suke ankarar da ita wani gyara idan buķatar hakan ta taso

Ya ce ķofar Hukumar a bude take ga duk wanda yaga wani gyara ko shawara ya sanar da Helkwatar Hukumar ta KAROTA ko ya same mu a kan Lambar Waya 08023608861 domin ciyar da aikin Hukumar da jihar Kano ta ɓangaren Sufuri gaba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending