News
An Sake Babban Rashi A Rundunar Sojin Nijeriya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Aƙalla sojojin Nijeriya shida sun riga mu gidan gaskiya sakamakon kwanton-ɓaunan da mayaƙan Boko Haram suka yi musu a hanyar Biu-Buni Yadi a Jihar Borno.
Daily Trust ta ruwaito cewa lamarin ya auku ne a ƙauyen Kamuya da ke kusa da Buratai, mahaifar tsohon Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Lt. Gen Tukur Buratai (mai murabus).
Rundunar ‘Yan Sanda Ta Tsinci Gawar Wata Budurwa Mai Shekaru 14, A Ban Dakin Wani Otel
Majiya ta kusa da rundunar tsaro ta ce, jami’an sun cimma ajali ne a kan hanyarsi ta zuwa Damaturu don shan mai.
“Abin baƙin ciki ne ainun, sojojin runduna ta 135 Special Force BN FOB ne da ke Buratai. An yi musu kwanton-ɓauna ne a hanyarsu ta zuwa shan mai a Damaturu, Jihar Yobe.
“Mun rasa babban janmi’ guda da direba da maharbi da wasu ‘yan rakiya huɗu, yayin da an kwashi waɗanda suka jikkata zuwa aisibiti inda ake yi musu magani,” in ji majiyar.
Wannan na zuwa ne mako guda da yin jana’izar wasu sojoji da masu tada ƙayar baya suka kashe a Jihar Delta a babbar maƙabarta dake Abuja.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
