News
Sai Na Yi Ƙarar Alƙalin Da Ya Yi Yunƙurin Daƙile Dawowar Sunusi- Gwamnan Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya sha alwashin kai ƙarar alƙalin da ya yi yunƙurin hana dawowar Sunusi,inda yace ta ya za ace Alƙali na ƙasar waje ya dinga katsalandan.
Gwamnan Ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani ga umarnin kotu da ta yi yinƙurin hana a dawo da Sanusi kan karagar mulki tare da hana tsige sarakuna biyar a jihar.
Da yake jawabi jim ƙadanbayan fitar da wasikar mayar da Alhaji Muhammadu Sanusi II a gidan talabijin na Africa House da ke gidan gwamnatin jihar Kano Gwamna Abba ya ce, “Alkalin da ya bayar da umarnin hana Dawowar Sunusi a Amurka ya ke zaune daga can ne yake bamu umurni , Wannan batu ai cin zarafi ne saboda haka dole ne in gabatar da shi a gaban Gwamna domin mu magance shi.”
