Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Kai Karar Gwamnonin Jihohin Kasar 36 Kara Gaban Kotun Koli

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Gwamnatin tarayya ta kai karar gwamnonin jihohin kasar 36 a gaban kotun koli, bisa zargin yin katsalandan a harkokin kananan hukumomi.

Advertisement

Premium Times ta ruwaito cewa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF) kuma Ministan Shari’a, Prince Lateef Fagbemi, ne ya shigar da karar don neman cikakken ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi, inda ya bayyana su a matsayin mataki na uku a gwamnatin kasar.

A cikin karar mai lamba SC/CV/343/2024, Ya bukaci kotun koli da ta haramtawa gwamnonin jahohi rusa zababbun shugabannnin kananan hukumomi da kuma nada masu kula da sha’anin mulkin kananan hukumomin ba bisa ka’ida ba.

Advertisement

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa irin wadannan ayyuka na gurgunta ‘yancin cin gashin kai da gudanar da ayyukan kananan hukumomi, wadanda suke da muhimmanci ga tsarin mulki da ci gaban kasa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending