Connect with us

News

Mun janye kalamanmu tare da bai wa Nuhu Ribadu hakuri —Gwamnatin Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnatin Kano ta ba wa Mashawarcin Shugaban Kasa kan sha’anin Tsaro Nuhu Ribadu hakuri kan zargin hannunsa a rikicin masarautun jihar.

Advertisement

Jaridar Inda Ranka ta ruwaito mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Aminu Abdulsalam a ranar Asabar yana zargi Ribadu da yunkurin dawo da Alhaji Aminu Ado Bayero kan kujerar Sarkin Kano bayan gwamnatin jihar ta sauke shi tare da sauran sarakunan jihar.

Mataimakin gwamnan Jahar Kano komarade aminu abdussalam ya Nemi afuwar Shugaban sojoji nuhu rubado

Daga bisani Ribadu ya nesanta kansa da kuma ofishinsa daga rikicin, sannan ya yi barazanar maka mataimakin gwamnan a kotu.

Advertisement

Bayan haka ne mataimakin gwamnan ya ba da hakuri ga Ribadu yana mai cewa yaudarar gwamnatin aka yi da bayanan da aka ba ta.

“Mun kara zurfafa bincike inda kuma gano cewa yaudarar mu aka yi, saboda haka, a madadin gwamnatin Kano, mana ba da hakuri ga Mashawarcin Shugaban Kasa kan Sha’anin Tsaro,” in ji mataimakin gwamnan.

Advertisement

Gwamnatin jihar ta kuma bukaci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya baki kada abin ya kara rincabewa fiye da haka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending