News
Karancin Ruwa: Akwai Gibi Na Lita Miliyan 200 Da Har Yanzu Ba A Magance Ba — Gwamnatin Kano
Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa har yanzu akwai gibi na lita miliyan 200 na ruwa da ba a magance ba, duk da gyare-gyaren da ake ci gaba da yi a bangaren samar da ruwa.
Kwamishinan Ruwa na jihar, Injiniya Haruna Doguwa, ne ya bayyana hakan yayin da yake bayani kan halin da ake ciki a fannin samar da ruwa ga al’ummar jihar kamar yanda Jaridar The Independent Mirror ta ruwaito.
Wasu Fusatattu Matasa Sun Kona Alkalin Wasan Ƙwallon ƙafa A Gaban Jama’a
Ya ce ko da an kammala gyaran cibiyoyin Wudil da Joda, da ake sa ran za su kara samar da ruwan daga lita miliyan 300 zuwa miliyan 500 a kullum, har yanzu hakan ba zai iya cike gibin bukatar ruwan da ake da shi ba.
“Jihar Kano na bukatar akalla lita miliyan 700 na ruwa a kullum, amma abin da ake iya samu yanzu bai wuce miliyan 300 ba. Idan aka kammala gyare-gyaren nan, za mu iya kai miliyan 500, amma akwai gibi na miliyan 200 da ba a cika ba,” in ji shi.
Kwamishinan ya ce wannan na nufin cewa wasu sassan jihar za su ci gaba da fama da matsanancin karancin ruwa, musamman a lokacin rani.
A yanzu haka, akwai unguwanni da dama da jama’a ke kwana suna neman ruwa, wasu kuma sai sun saye da tsada, wanda hakan ke kara jefa su cikin mawuyacin hali.
