Politics
Jam’iyyar APC Ta Shirya Shiga Zaben Shugabannin Kananan Hukumomi da Kansiloli A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Jam’iyyar APC reshen Jihar Kano Karkashin Jagorancin Abdullahi Abbas, ta bukaci al’ummar Kano da mambobin jam’iyyar da suke sha’awar tsayawa takarar shugabancin ƙaramar hukuma da Kansila da su miƙa takardar sha’awarsu ga ofisoshin jam’iyyar dake Kananan Hukumominsu.
Jam’iyyar na sanar da cewar tun daga ranar 12 zuwa 14 ga watan Satumba Ofisoshin jam’iyyar APC su kasance a buɗe domin karɓar masu sha’awar tsayawa takara, tun daga karfe 8 na safe zuwa 5 na yamma.
Sanarwa na dauke dasa hannun Hon. Ahmad S. Aruwa, Kakakin Jam’iyyar APC na Kano.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
