Connect with us

News

Dan Majalisar Tarayya Na Gaba-gaba A Kwankwasiyya Ya Fice Daga Tafiyar

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Dan majalisar tarayya mai wakilar karamar hukumar Dala a jihar kano, Aliyu Sani Madakin Gini ya bayyana ficewarsa daga tafiyar Kwankwasiyya dake biyayya da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Advertisement

Idan za a iya tunawa Aliyu Sani Madakin Gini na daga cikin na gaba-gaba a tafiyar Kwankwasiyya da yiwa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso biyayya.

Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Rigakafin Cutar Shan Inna

Madakin Gini ya bayyana ficewarsa tasa ne daga tafiyar Kwankwasiyya da yammacin wannan rana ta lahadi a mazabar ta Dala dake jihar kano.

Advertisement

“Daga yau Ni Aliyu Sani Madaki na bar tafiyar Kwankwasiyya, Saboda Kwankwasiyya yaudara ce, Kwankwasiyya cin amana ce, Mai girma Gwamnan jihar Kano Alh. Abba Kabir Yusif mutumin kirki ne, ina baka shawara ka tsaya da kafarka ka da aje fa ka wani rami da bazan bayyana shi yanzu ba”. Inji Ali Madaki.

Ya ce ya shirya tsaf domin tallafawa duk wanda ya biyo shi, yace kowa zai amfana, ya yi alkawarin zai share sama da Kwana 7 domin ganawa da magoya bayansa.

Advertisement

Ya umarci duk wani wanda ya yarda cewa shi ne Jagoransa, ya cire jar hula da jajayen mayafai.

Sai dai dan majalisar bai bayyana ficewarsa daga jam’iyyar NNPP ba.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending