News
Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Rigakafin Cutar Shan Inna
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Gwamnatin jihar Kano a karkashin ma’aikatar lafiya, ta kaddamar da rigakafin cutar shan inna a karamar hukumar Ungogo, saboda yawan al’ummar yankin da kuma tarihin bullar cutar.
Dokta Abubakar Labaran yusif, ya bayyana dalilin kaddamar da rigakafin cutar shan inna a kamar Hukumar Ungogo, ya ce karamar hukumar na da adadin yara masu yawa
Bayan Hukuncin CAF An Fara Kamen ’Yan Najeriya A Kasar Libya
Ya kara da cewa Ungogo na fuskantar barkewar cututtuka masu yaduwa kamar kwalara da cutar Mashako.
A nasu jawabin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) sunusi mayana ta nuna damuwarta kan yadda cutar shan inna ke ci gaba da wanzuwa.
Dakta Mayana, ta yi jawabi ne a taron gangamin yaki da cutar shan inna ta 0 a karamar hukumar Ungogo, ta sha alwashin fadada hanyoyin da za a wayar da kan jama’a domin kawar da cutar.
“Muna kashe makudan kudade domin ganin an kawar da wannan cutar amma abin mamaki duk shekara muna yin wannan gangami amma ba mu cika sharuddan da ake bukata ba, don haka a wannan karon a shirye muke mu yaki wannan cutar ta Shan Inna ba tare da gajiyawa ba don ganin cewa Kano ta samu ‘yanci.
Alh Abdulkadir magajin malam hakimin karamar hukumar Ungogo ya yi kira ga iyaye da su fito da ‘ya’yansu domin karbar allurar rigakafin cutar.
Sai dai ya yabawa gwamnatin jiha karkashin jagorancin Engr Abba kabar yusif bisa kokarin da yake yi na magance cututtuka masu yaduwa da marasa yaduwa.
Jihar na da burin yi wa yara miliyan 3.6 allurar rigakafin shekaru kasa da shekaru 5 a fadin kananan hukumomi 44.
