Connect with us

News

Ana Zargin Miji Da Kone Matarsa Da Fetur Akan Sabani

Published

on

Wata Budurwa Ta Cinna Wa Kanta Wuta A Ofishin ‘Yan Sanda Saboda Saurayin Ta Ya Yi Aure

DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

Wani mutum mai shekaru 55 mai suna Olubunmi Johnson, ya shiga hannun ‘yansandan Jihar Ogun, bisa zargin kone matarsa da wuta a yankin Ota.

LEADERSHIP HAUSA ta ruwaito cewa lamarin ya faru misalin karfe 8:30 na daren ranar Juma’a, bayan wata sabani ya barke tsakanin ma’auratan a gidansu da ke kan titin Fagbuyi, Ilogbo.

Ana Zargin Miji Da Kone Matarsa Da Fetur Akan Sabani

Ana zargin Johnson da zuba wa matarsa mai suna Kikelomo fetur sannan ya cinna mata wuta.

Kakakin ‘yansandan jihar, Omolola Odutola ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin.

Ta ce iyalan matar sun sanar wa ‘yansanda faruwar lamarin.

Advertisement

 

Odutola ta kara da cewa, duk da har yanzu ba a san musabbabin sabanin ba, amma an garzaya da matar asibiti.

Ta bayyana cewa an kama Johnson, kuma ‘yansanda na bincike kan lamarin a matsayin yunkurin kisa.

“Jami’an ‘yansanda daga ofishin Ilogbo sun yi gaggawar daukar mataki, inda suka kama wanda ake zargi mai shekaru 55.

“Shaidu sun garzaya da matar zuwa asibiti bayan ya cinna mata wuta,” in ji Odutola.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending