Connect with us

News

Yan Sanda Sun Kama Wata Mota Ɗauke Da Ƙananan Yara 59 Da Ake Zargin Sato Su Aka Yi

Published

on

Yan Sanda Sun Kama Wata Mota Ɗauke Da Ƙananan Yara 59 Da Ake Zargin Sato Su Aka Yi

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ta kama wasu yara maza 59 da ake zargi anyi safarar su ta hannun ‘yan sintiri da masu gadi

Advertisement

Kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, Olatunji Disu, ya bayyana cewa an gano yaran masu shekaru tsakanin 4 zuwa 12 ba tare da cikakkun takardu ko amincewar iyaye ba.

Bincike na Gaskiya: Shin Hukumar Kwastam ta Nijeriya Ta Nuna Bangaranci a Karin Girma ga Jami’ai Daga Arewa?

Jaridar KANO TIMES ta ruwaito cewa lamarin da ya haifar da fargabar cin zarafin yara da safarar su.

Advertisement

“A ranar 6 ga watan Janairun 2025, da misalin karfe 15 : 30, wata tawaga karkashin jagorancin mataimakin Sufeton ‘yan sanda (DSP) Sarki Umar ta tare wata farar motar kirar Peugeot 15 tare da Reg. No. KMC 283 ZJ a kan hanyar Abuja zuwa Kano.

“An gano motar bas din tana jigilar yara maza 59 masu shekaru tsakanin 4 zuwa 12. Binciken farko ya nuna cewa yaran da suka fito daga iyalai daban-daban, wani mutum mai suna Idris Usman, mazaunin jihar Nasarawa ne ke jigilar su. Ya yi tattaki zuwa jihar Kano ne domin tara yaran kan hanyar zuwa jihar Nasarawa da nufin horar da su,”

Advertisement

Rundunar ‘yan sandan ta baiwa jama’a tabbacin gudanar da cikakken bincike a kan lamarin domin gano cikakken aikin da kuma tabbatar da tsaron yaran.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending