News
Trump Zai Rushe Wasu Hukumomi, Ciki Har Da VOA
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya rattaba hannu kan sabuwar doka da za ta takaita ayyukan wasu hukumomi guda shida tare da rushe wasu gaba daya, ciki har da kafar yada labarai ta Voice of America (VOA).
Hukumomin da abin ya shafa sun hada da gidajen adana kayan tarihi, dakunan karatu, da bangaren kula da marasa galihu. A cewar Trump, wadannan hukumomi na yada bayanai da ke nuna masa kyara.
Kwamitin Tabbatar Da Tsaro A Kano Ya Kaddamar Da Gagarumin Samame Kan ‘Yan Daba Da Masu Shaye-shaye
Sabuwar daraktar da za ta jagoranci wannan rushewa ita ce ‘yar jarida Kari Lake, wadda aka nada domin aiwatar da sabon tsarin. VOA, wacce aka kafa shekaru 80 da suka wuce, na yada shirye-shiryenta a harsuna 40 ta rediyo, talabijin, da intanet.
Matakin ya jawo cece-kuce, inda masu sukar sa ke ganin hakan a matsayin yunkuri na dakile ‘yancin yada labarai a Amurka.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News1 day ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
