Connect with us

News

Titin Jirgin Ƙasa Daga Legas Zuwa Kano Zai Fara Aiki —Hukumar NRC

Published

on

Railway

 

Hukumar Kula da Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa ta kammala shirye-shiryen fara jigilar kaya ta layin dogo mai ƙaramin faɗi tsakanin jihohin Lagos da Kano.

Manajan Daraktan NRC, Kayode Opeifa, ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da yake duba tashar jirgin ƙasa ta Dugbe a Ibadan, Jihar Oyo. Ya ce hukumar tana da ƙwarin gwiwar dawo da jigilar kaya a wannan shiyya tare da ƙaddamar da tashar Dugbe da zarar an fara aiki.

Shugaba Tinubu Na Shirin Naɗa Sabon Shugaban Hukumar INEC

Opeifa ya kuma buƙaci ma’aikatan NRC da su ƙara ƙoƙari wajen bunƙasa kuɗaɗen shiga, yana mai cewa ƙarin kuɗin da aka samu zai taimaka wajen kyautata albashi da walwalar ma’aikata.

Dangane da matsalar satar kayayyakin jirgin ƙasa, ya nanata cewa NRC ba ta da kayan da suka zama tarkace, yana mai bada umarni ga jami’an tsaro da su kama duk wanda aka samu yana lalata kayayyakin hukumar.

A yayin ziyarar, Darakta-Janar na Development Agenda for Western Nigeria (DAWN), Seye Oyeleye, ya bayyana cewa suna da shirin haɗa kai da NRC don farfaɗo da jigilar jama’a a yankin kudu maso yamma.

Advertisement

 

 

SOLACEBASE

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending