Connect with us

News

Janar Tsiga Ya Kuɓuta Bayan Kwana 56 A Hannun ‘Yan Bindig

Published

on

Maharazu Tsiga 800x500

Birgediya Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), tsohon darakta Janar na shirin NYSC, ya samu ‘yanci bayan shafe kwanaki 56 a hannun ‘yan bindiga. An sace shi ne a garinsu da ke ƙaramar hukumar Bakori a Jihar Katsina ranar 5 ga Fabrairu, tare da wasu mutum tara.

Bayan biyan kuɗin fansa, masu garkuwa sun ƙi sakin shi nan take, inda suka ci gaba da tsare shi har na tsawon makonni. Akwai rashin jituwa kan adadin kuɗin da aka biya, inda wasu ke cewa Naira miliyan 60 aka biya, yayin da wasu majiyoyi ke cewa adadin ya ninka hakan sau uku. Majiyar daga danginsa ta bayyana cewa bayan an miƙa kuɗin, masu garkuwar sun ɗauki mako guda kafin su kira danginsa tare da ba su damar jin muryarsa.

Kwacen Waya Da Fadan Daba Ya Haifar Da Zaman Dardar A Unguwanni Da Dama A Cikin Kano

Wani babban jami’in soja ya tabbatar da sakin Tsiga, yana mai cewa yana cikin ƙoshin lafiya. Haka nan, wasu majiyoyi daga danginsa sun bayyana cewa an sako shi daga Jihar Zamfara, kuma ana shirin kai shi Abuja. Wannan na zuwa ne bayan an ƙi ƙara biyan kuɗin fansa da ‘yan bindigar suka buƙata a ƙarin lokaci.

 

 

 

Advertisement

BLUEPRINT 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending