News
Janar Tsiga Ya Kuɓuta Bayan Kwana 56 A Hannun ‘Yan Bindig
Birgediya Janar Maharazu Tsiga (mai ritaya), tsohon darakta Janar na shirin NYSC, ya samu ‘yanci bayan shafe kwanaki 56 a hannun ‘yan bindiga. An sace shi ne a garinsu da ke ƙaramar hukumar Bakori a Jihar Katsina ranar 5 ga Fabrairu, tare da wasu mutum tara.
Bayan biyan kuɗin fansa, masu garkuwa sun ƙi sakin shi nan take, inda suka ci gaba da tsare shi har na tsawon makonni. Akwai rashin jituwa kan adadin kuɗin da aka biya, inda wasu ke cewa Naira miliyan 60 aka biya, yayin da wasu majiyoyi ke cewa adadin ya ninka hakan sau uku. Majiyar daga danginsa ta bayyana cewa bayan an miƙa kuɗin, masu garkuwar sun ɗauki mako guda kafin su kira danginsa tare da ba su damar jin muryarsa.
Kwacen Waya Da Fadan Daba Ya Haifar Da Zaman Dardar A Unguwanni Da Dama A Cikin Kano
Wani babban jami’in soja ya tabbatar da sakin Tsiga, yana mai cewa yana cikin ƙoshin lafiya. Haka nan, wasu majiyoyi daga danginsa sun bayyana cewa an sako shi daga Jihar Zamfara, kuma ana shirin kai shi Abuja. Wannan na zuwa ne bayan an ƙi ƙara biyan kuɗin fansa da ‘yan bindigar suka buƙata a ƙarin lokaci.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
