News
DA ƊUMI-ƊUMI: Pakistan Za Ta Dauki Fansa Kan Harin Sama Da India Ta Kai
Aƙalla mutane bakwai ne suka rasa rayukansu, ciki har da yara ƙanana, sakamakon wani hari da India ta kai ta sama a wani yanki na Pakistan da daddare a jiya Litinin.
Rahotannin da gidan talabijin na gwamnati a Pakistan ya fitar sun bayyana cewa rundunar sojin ƙasar ce ta tabbatar da harin, inda ta ce India ta harba makamai masu linzami a wani yanki da ke arewacin ƙasar.
‘Yan Bindiga Na Cin Karensu Babu Babbaka A Shanono Da Bagwai – Dan Majalisa
Baya ga mutanen da suka mutu, wasu da dama sun samu raunika, kuma jami’an agajin gaggawa na ci gaba da aikin ceto a yankin da abin ya faru.
Gwamnatin Pakistan ta bayyana cewa za ta dauki fansa a “lokaci da wuri da suka dace”, tana mai zargin India da keta hurumin ƙasar da kuma tayar da zaune tsaye.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da dangantaka ke ƙara tsami tsakanin ƙasashen biyu da ke da makaman nukiliya, musamman a kan rikicin yankin Kashmir da ke janyo ce-ce-ku-ce tsakanin New Delhi da Islamabad.
Kawo yanzu dai babu wani jawabi daga hukumomin India dangane da harin.
