Connect with us

News

ASUU Ta Ce Za Ta Maka JAMB Kotu Kan Mummunan Sakamakon UTME

Published

on

images (4)

Kungiyar Malaman Jami’a ta Kasa (ASUU), reshen Jami’ar Nsukka (UNN), ta bayyana cewa za ta dauki matakin shari’a a kan Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Makarantun Gaba da Sakandare ta Kasa (JAMB), saboda yadda dalibai da dama – musamman na Kudu Maso Gabas – suka fadi jarabawar UTME ta bana.

Shugaban ASUU na UNN, Kwamared Oyibo Eze, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a garin Nsukka da ke Jihar Enugu a ranar Laraba.

Advertisement

Kungiyoyin Farar Hula 107 Sun Goyi Bayan Dakatar Da Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye A Kafafen Yada Labarai A Kano

Kwamared Eze ya ce, “Shiyyar da ta fi fuskantar faduwa a jarabawar UTME ita ce Kudu Maso Gabas. Wannan wani nau’i ne na gangan da JAMB ke yi domin hana yaran wannan yanki damar shiga jami’o’in kasar nan.”

Ya ce ASUU za ta kalubalanci sakamakon a kotu idan har JAMB ta gaza sake duba lamarin da kuma ba daliban da suka cancanta makin da ya dace.

Advertisement

“Ofishina ya cika da koke-koken iyaye da dalibai kan yadda aka danne su a wannan sakamako. Ba za mu yi shiru ba,” in ji shi.

Kwamared Oyibo ya kuma bukaci gwamnonin jihohin Kudu Maso Gabas da su tashi tsaye domin kare ‘ya’yan jiharsu, yana mai cewa ya kamata a dauki matakin gaggawa domin dakile abin da ya kira rashin adalci da wariya a fagen ilimi.

Advertisement

A gefe guda kuwa, shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana cewa hukumar na shirin sake gudanar da jarabawa ga wasu daliban da ke jihohin Kudu Maso Gabas da kuma Legas.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending