News
An Sanya Ladan Naira Miliyan 5 Ga Wanda Ya Bankado Fursunonin Da Suka Tsere
Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya ta bayyana bayar da ladan Naira miliyan biyar ga duk wanda ya bayar da sahihin bayani da zai kai ga kamo fursunonin da suka tsere daga gidan gyaran hali na Ilesha da ke Jihar Osun.
Wata sanarwa da Mataimakin Kwamanda kuma Jami’in Hulda da Jama’a na hukumar, Umar Abubakar ya fitar a ranar Laraba ta ce fursunoni bakwai ne suka tsere daga gidan gyaran halin, kuma ana ci gaba da bincike don gano inda suka shiga.
Hukumar ta bukaci jama’a da su taimaka wajen samar da duk wani bayani da zai taimaka wa jami’an tsaro kama fursunonin, tana mai tabbatar da cewa za a kiyaye sirrin wadanda suka bayar da bayanan.
An fadi cewa jama’a za su iya tuntubar hukumar ta hanyar imel kamar haka:
complaintresponsedesk@corrections.gov.ng
info@corrections.gov.ng
Hukumar ta ce hadin kan jama’a na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a cikin kasa.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
