Connect with us

News

An Sanya Ladan Naira Miliyan 5 Ga Wanda Ya Bankado Fursunonin Da Suka Tsere

Published

on

FB IMG 1747904199033

Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya ta bayyana bayar da ladan Naira miliyan biyar ga duk wanda ya bayar da sahihin bayani da zai kai ga kamo fursunonin da suka tsere daga gidan gyaran hali na Ilesha da ke Jihar Osun.

Wata sanarwa da Mataimakin Kwamanda kuma Jami’in Hulda da Jama’a na hukumar, Umar Abubakar ya fitar a ranar Laraba ta ce fursunoni bakwai ne suka tsere daga gidan gyaran halin, kuma ana ci gaba da bincike don gano inda suka shiga.

Advertisement

An Gano Hamdiyya A Zamfara Cikin Mawuyacin Hali

Hukumar ta bukaci jama’a da su taimaka wajen samar da duk wani bayani da zai taimaka wa jami’an tsaro kama fursunonin, tana mai tabbatar da cewa za a kiyaye sirrin wadanda suka bayar da bayanan.

An fadi cewa jama’a za su iya tuntubar hukumar ta hanyar imel kamar haka:

Advertisement

complaintresponsedesk@corrections.gov.ng

info@corrections.gov.ng

Advertisement

Hukumar ta ce hadin kan jama’a na da matukar muhimmanci wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a cikin kasa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending