Connect with us

News

Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Trump Na Hana Jami’ar Harvard Daukar Daliban Waje

Published

on

Trump

Wata kotu a Amurka ta dakatar da matakin  Shugaban Amurka, Donald Trump, na hana Jami’ar Harvard daukar dalibai daga kasashen waje.

Alkalin kotun gunduma, Allison Burroughs, ce ta yanke hukuncin bayan jami’ar ta garzaya kotu tana kalubalantar matakin gwamnatin Trump na dakatar da shirin musayar dalibai daga waje.

Advertisement

FCTA Ta Ƙwace Filin Sakatariyar PDP Da Wasu Filaye 4,793 A Abuja

Harvard ta ce matakin gwamnatin tamkar ramuwar gayya ne saboda jami’ar ta ki goyon bayan wasu manufofin Trump da ake ganin sun nuna wariya ga ‘yan kasashen waje, musamman baki.

Trump ya sha sukar jami’ar bisa kin bin tsarin sa na sa ido kan baki, inda ya zarge ta da zama mafakar masu kyamar Yahudawa.

Advertisement

Har ila yau, ya sha alwashin cire kudaden tallafi daga jami’ar, wanda ya kai dala biliyan tara, da kuma fitar da wani masanin kimiyya daga sashen kiwon lafiyarta.

Harvard na daya daga cikin manyan jami’o’in duniya da suka fi fitar da mutane da suka yi fice a fannoni daban-daban, ciki har da wadanda suka ci kyautar Nobel fiye da sau 160.

Advertisement

Hukuncin kotun ya kawo karshen kokarin Trump na dakile daukar daliban waje a jami’ar da ke da suna a fadin duniya.

 

Advertisement

 

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending