Connect with us

News

JAMB Ta Saki Sakamakon Ɗaliban Da Suka Sake Rubuta Jarrabawa

Published

on

jamb exam1 (1)

Hukumar Shirya Jarrabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ta fitar da sakamakon ɗaliban da suka sake rubuta jarabawar UTME ta bana.

JAMB ta ce an sake jarrabawar ce saboda tsaikon da ya faru lokacin da aka fara jarrabawar a watan da ya gabata, musamman a wasu cibiyoyi a Legas da jihohin Kudu maso Gabas.

Advertisement

JAMB: Hukuma Ta Kama Mutum 20 Bisa Zargin Kutse A Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Dr. Fabian Benjamin, ya fitar ranar Lahadi, ya ce ɗalibai 336,845 ne aka sake ba damar rubuta jarrabawar, amma daga cikinsu, 21,082 ba su halarta ba.

Ya kuma ce hukumar ta gano wasu ayyukan satar jarrabawa da ɗalibai da wasu cibiyoyin jarrabawa ke aikatawa, kuma tuni an fara daukar mataki a kai.

Advertisement

JAMB ta ce ta sake shirya jarrabawar ne domin tabbatar da adalci ga ɗaliban da suka fuskanci matsala, da kuma tabbatar da cewa kowa ya samu damar daidai wajen nuna abin da ya koya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending