Connect with us

Politics

Kwankwaso Na Fakewa da Talakawa Domin Cimma Burinsa,  – Adnan Mukhtar

Published

on

Adnan Mukhtar

Wani ɗan gwagwarmaya kuma masani a fagen siyasa, Comrade Adnan Mukhtar, ya bayyana cewa siyasar Najeriya ta fi karkata kan muradun kai na ‘yan siyasa, ba wai muradin talakawa ba kamar yadda ake ikirari.

A cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Adnan ya bayyana cewa tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, na amfani da sunan talakawa ne kawai a matsayin garkuwa domin cimma muradin kansa na siyasa.

NAPTIP Na Neman Speed Darlington Ruwa a Jallo Kan Zargin  Cin Zarafi A Intanet

“Kwankwaso ba ya adawa da Tinubu saboda cire tallafin fetur ko tsadar rayuwa da ke addabar mutane ba, illa kawai saboda yana kallon Tinubu a matsayin babban cikas ga burin siyasarsa,” in ji Adnan.

Ya ce siyasar Najeriya ta koma wata hanya ta son zuciya da kare muradin kansu na kai, inda ya yi zargin cewa Kwankwaso yana iya haɗa kai da Tinubu a kowane lokaci idan hakan zai amfani burin sa.

Adnan ya ƙara da cewa: “Idan har Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai zaɓi mataimaki daga Arewa a zaben 2027, akwai yiwuwar ya zaɓi Rabiu Musa Kwankwaso ko Sanata Barau Jibrin. Wannan shi ne yadda siyasar Najeriya ke tafiya yanzu.”

Ya bayyana cewa mafi yawan ‘yan siyasa na amfani da kalmar “talaka” ne kawai domin jawo hankalin jama’a, amma a zahiri ba su da wata damuwa da jin daɗin rayuwar talakawa.

Advertisement

“A zahiri, siyasar Najeriya siyasar kai ne, ba siyasar talaka ba,” in ji shi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending