News
Ƙungiyar ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU), ta yi gargaɗi cewa za ta iya sake tsunduma yajin aiki saboda gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗauka.
Shugaban ƙungiyar, Christopher Piwuna, ya ce gwamnati ba ta kula da walwalar malamai, ba ta samar da kuɗaɗen gudanar da jami’o’i yadda ya kamata, kuma ba ta aiwatar da yarjejeniyar da suka cimma ba.
Wannan na zuwa ne bayan Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana cewa “Babu wata jami’a ko malaman ASUU da za su sake shiga yajin aiki” idan aka ci gaba da tattaunawa da kuma cika buƙatun malaman.
Sai dai ASUU ta ce hanyar da za a guji yajin aiki ita ce kawai a cika musu alƙawuran da aka riga aka amince da su.
Ƙungiyar ta bayyana cewa yawancin malamai suna koyarwa da gudanar da bincike ba tare da kayan aiki ko tallafi ba.
Wasu ma ba sa iya biyan kuɗin mota zuwa wajen aiki, biyan buƙatun yau da kullum, har ma da kuɗin makarantar ’ya’yansu.
AMINIYA
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
