Connect with us

News

Yan Bindiga Sun Hallaka Jami’in Sa-kai, Sun Sace Matan Fitaccen Dan Kasuwa A Kano

Published

on

Wasu ƴan bindiga sun kai hari a garin Kafin Maiyaki da ke ƙaramar hukumar Kiru, jihar Kano, inda suka kashe wani jami’in sa-kai sannan suka yi garkuwa da matan wani fitaccen ɗan kasuwa a yankin.

Shaidun gani da ido sun ce maharan sun kai samame gidan Alhaji Ibrahim Ahmad Rufai, shugaban ƙungiyar ƴan kasuwar Kafin Maiyaki, inda suka yi awon gaba da matansa zuwa wurin da ba a sani ba.

Advertisement

BBC Hausa Ta Ƙi Karɓar Ajiye Aikin Shugabanta Aliyu Tanko, Ta Dakatar da Shi Tsawon Watanni Uku

A yayin harin, wani ɗan sa-kai da ya yi ƙoƙarin kare al’umma daga farmakin maharan ya rasa ransa.

Wani masani kan tsaro a yankin, Bakatsine, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis ta hanyar wallafa sanarwa a shafinsa na X.

Advertisement

Har zuwa lokacin kammala wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa kanharin ba.

 

Advertisement

 

DAILY POST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending