News
Da Dumi-Dumi: Shugaba Tinubu ya sanar da kawo karshen dokar ta-baci a Jihar Ribas
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cewa dokar ta-baci da ya ayyana a Jihar Ribas ta ƙare, kuma ba za a tsawaita ta ba.
Tinubu ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar daga fadar shugaban ƙasa a yau Laraba, 17 ga Satumba, 2025.
Da Dumi-Dumi: Ba zan tsawaita dokar ta bacin da na sanya a jihar Rivers ba – Shugaba Tinubu
Ya tunatar da cewa an ayyana dokar ta-bacin ne a ranar 18 ga Maris, 2025, sakamakon rikicin siyasa da ya durƙushe harkokin gwamnati a Ribas.
A cewar shugaban ƙasa, rikicin ya samo asali ne daga rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin jihar, inda aka rarrabu gida biyu – wasu huɗu na tare da gwamna, yayin da sauran 27 suka tsaya kan kakakin majalisar, Martins Amaewhule.
Tinubu ya ce wannan rabuwar kawunan ya jefa jihar cikin rikicin mulki, wanda har kotun koli ta tabbatar da cewa babu ingantacciyar gwamnati a Ribas a lokacin.
Sai dai a cewar shugaban ƙasa, cikin watanni shida da dokar ta-bacin ta ɗauka, an samu sabon yanayi na fahimtar juna tsakanin ɓangarorin siyasar jihar.
Ya ce daga ranar Alhamis, 18 ga Satumba, 2025, gwamna, mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar za su koma bakin
-
News7 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News7 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
