Connect with us

News

Jami’an Ƴansanda Sun Dakile Yunkurin Sace Jariri Da Wasu Ma’aikatan Asibiti A Jigawa

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Jigawa ta sanar da samun gagarumar nasara a yaƙi da aikata laifuka, inda jami’anta suka dakile wani yunƙurin fashi da makami tare da kama wasu da ake zargi da sace wani jariri.

Mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya bayyana cewa da misalin ƙarfe 3:00 na safiyar Alhamis, jami’an Sashen Yaƙi da Manyan Laifuka (VCRU) sun yi artabu da wasu da ake zargin ‘yan fashi ne a unguwar Danmasara da ke Dutse.

ICPC Ta Bankado Sabbin Hukumomin Bogi Biyu Yayin Bincike Kan PFIPC ‎

Bayan bin motarsu da suka yi, waɗanda ake zargin sun bude wa jami’an wuta kafin su tsere cikin daji. Daya daga cikinsu ya samu raunuka kuma ya rasu a asibiti, yayin da aka kwato adduna biyu, sanduna uku, igiyoyi da wayar salula.

A wani samame na daban, rundunar ta ceto wani jariri mai shekara ɗaya da rabi da aka sace daga Asibitin Babura.

An kama Khadija Aliyu mai shekaru 20 da jaririn a hannunta, sannan bincike ya kai ga cafke Sadik Sale Yahaya, ma’aikacin jinya a Asibitin Babura, bisa zargin haɗa baki wajen satar jaririn.

Advertisement

Wacce ake zargin ta amsa cewa ta yi shirin sayar da jaririn kan kuɗi Naira miliyan biyu.

Rundunar ta ce an tsare jaririn cikin aminci kuma za a mayar da shi ga iyayensa bayan kammala bincike.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Jigawa, CP Tijjani Murtala, ya yaba da ƙwazon jami’an tare da ƙarfafa gwiwar al’umma su ci gaba da bai wa rundunar sahihan bayanai domin yaƙi da aikata laifuka.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending