Connect with us

News

Sai ’Yan Takara Sun Biya N10m Kafin Wallafa Fosta —Gwamnatin Kogi

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya rattaba hannu kan dokar tilasta wa ’yan takarar shugaban kasa a zabe mai zuwa biyan Naira miliyan 10 kafin kowannensu a ba su izinin nuna fosta da allunan talla a jihar.

 

Advertisement

Dokar ta wajabta wa ’yan takarar gwamna biyan Naira miliyan biyar, masu takarar Sanata kuma Naira miliyan biyu, ’yan takarar Majalisar Wakilai Naira miliyan daya, sai ’yan takarar Majalisar Dokokin jiha Naira 500,000.

 

Advertisement

 

Sabuwar dokar tallace-tallace ta shekara ta 2022 na daga cikin wasu kudirori uku da gwamnan ya rabbata hannu a kai domin su zama doka a jihar.

Advertisement

 

Gwamna Bello ya ce sababbin dokokin da aka sanya wa hannu za su taimakawa wajen tabbatar da tsaftar muhalli da karuwar kudaden shiga.

Advertisement

 

Yahaya Bello ya bukaci ’yan majalisar dokokin jihar da su zakulo duk wasu dokokin da aka sanya wa hannu a baya, amma ba a aiwatar da su a ma’aikatu ko hukumomin jihar domin a hada gwiwa da sa ido wajen aiwatar da su da tantancewa.

Advertisement

 

Gwamnan ya kuma bukaci majalisar ta ci gaba da yin aiki tare da sauran bangarorin gwamnati domin yi wa al’umma hidima.

Advertisement

 

Sauran dokoki da aka rattabawa hannu sune Dokar sokewa da sake fasalin otal da Hukumar Yawon shakatawa na 1995; da dokar Kafa Hukumar Kula da yawon bude ido ta Jihar Kogi da sauran batutuwan da suka shafi hakan.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending