Connect with us

News

Mun Gano Kayan Sojoji Da Tarin Kudade A Gidan Tukur Mamu – DSS

Published

on

Tukur Mamu

DAGA KHADIJA ABDULLAHI MUHMD

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Hukumar Tsaro ta DSS ta ce ta kama kayayyakin da suka hada da kakin sojoji da kudaden kasashen waje da dama a gidan Tukur Mamu, dan jaridar nan da ke shiga tsakani da ’yan bindiga.

Advertisement

 

Kakakin hukumar ta DSS, Peter Afunanya ne ya bayyana hakan lokacin da yake tsokaci a kan sakamakon binciken da suka yi a gidan mawallafin jaridar nan ta Desert Herald da sanyin safiyar Alhamis.

Advertisement

Yajin aikin ASUU: Dalibin da yake shekarar karshe karatun digiri ya koma dillalan abin

DSS ta kuma ce ta kama abubuwa da dama a gidan, kuma da zarar ta kammala bincike za ta maka shi a agaban kotu.

Advertisement

 

A cewar Afunanya, “Yanzu haka, jami’an tsaron sun samu izinin bincike gidansa da ofishinsa, kuma a nan ne aka sami irin wadannan kayayyakin.

Advertisement

 

“Sauran kayayyakin sun hada da kudaden kasashen waje daban-daban da abubuwan hada-hadar kudi.

Advertisement

 

“Yayin da muke ci gaba da bincike, tabbas za mu gurfanar da shi a gaban kuliya,” inji Kakakin na DSS.

Advertisement

 

A ranar Laraba ce dai hukumar ta cafke Tukur Mamu a filin jirgin sama na Kano, bayan ta sa an tiso mata keyarshi daga kasar Masar.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending