Connect with us

News

Ebola ta sake hallaka ma’aikacin lafiya a Uganda

Published

on

Cibiyar kula da lafiya

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Ma’aikatar lafiya ta Uganda ta tabbatar da mutuwar wata ma’akaciyar lafiya, wadda ke aikin allurar hana radadin ciwo yayin da za a yi wa mutum tiyata.

Advertisement

 

Sanarwar da Ministar Lafiya Jane Ruth Aceng ta fitar ta ce, Margaret Nabisubi, mai shekara 58, ta rasu ne cikin daren da ya gabata, wayewar garin Larabar nan.

Advertisement

Hukumar ‘Yan Sanda Ta Kori Manyan Jami’ai 7, Ta Rage Matsayin Wasu 10

Wasu ma’aikatan lafiya sun samu kansu cikin hadarin kamuwa da kwayar cutar lokacin da suka yi wa mutum na farko da ya kamu da cutar, wanda za a yi masa tiyata, daga nan ne aka kwantar da su a asibitin yanki na Fort Portal.

Advertisement

 

Wani dalibi dan kasar Tanzania da ke koyon aikin likita, wanda na daga cikin ma’aikatan shi ma ya rasu a karshen mako.

Advertisement

 

Haka shi ma wani karamin ma’aikacin lafiya a gundumar Kagadi wanda ba ya cikin wancan ayarin shi ma cutar ta hallaka shi.

Advertisement

 

Sannan ana zargin cutar ta Ebola kuma ta kashe wata ungozoma duk a cikin ‘yan kwanakin nan a kasar ta Uganda.

Advertisement

 

Ma’aikatan lafiya na korafin rashin isassun kayan aiki na kariya a farkon kwanakin barkewar cutar.

Advertisement

 

Alkaluman da hukuma ta fitar sun nuna cewa mutum 43 ne suka kamu da cutar tun bayan da ta barke mako biyu da ya gabata kuma 10 daga cikinsu sun mutu.

Advertisement

 

Jami’an lafiya sun ce sun gano sama da mutum 800 da ake zargin sun yi mu’amulla da wadanda kwayar cutar ta harba.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

BBC NEWS

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending