News
Barazanar Harin Ta’addanci Ta Jawo Rufe Kasuwanni A Neja
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Barazanar harin ta’addanci ta tilasta masarautar Borgu da ke Karamar Hukumar Borgu ta Jihar Neja rufe manyan kasuwannin yankin.
Masauratar ta ce ta dauki wannan matakin ne domin kare rayukan jama’ar yankin daga ayyukan ‘yan ta’adda..
Abin da ya jawo faɗa tsakanin Murtala Garo da Ado Doguwa
Wannan na zuwa ne biyo bayan harin da ‘yan bindiga suka kai sansanin sojojin da ke Wawa, daura da tafkin Kainji, a ranar Asabar.
Cikin wata sanarwar da ta fitar ta hannun Shugaban Kungiyar Matasan yankin, Muhammad Kabir, Masarautar ta ce ganin yadda zaman dar-dar ke dada kamari a tsakanin mazauna yankin ya sa aka dauki matakin rufe manyan kasuwannin yankin don kauce wa hare-haren ta’addanci.
Kazalika, masarautar ta kafa dokar hana fita daga karfe 9:00 na safe zuwa 6:00 na yamma don takaita zirga-zirgar jama’a a yankin.
Kazalika, ta ce daga yanzu tilas masu ababen hawa a yankin su tabbatar sun yi wa ababen hawan nasu lamba ko kuma a raba su da su.
Dokar takaita zirga-zirgar da kuma umarnin tabbatar da yi wa ababen hawan lamba sun soma aiki ne daga ranar Litinin, 31 ga watan Oktoba, in ji sanarwar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
