Connect with us

News

Motar Yashi Ta Muttsuke Mutum 6 A Adamawa

Published

on

Wani hatsarin mota

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wata babbar motar yashi ta muttsuke mutum shida har lahira, ciki har da wani mai ba da hannu a garin Yola, Jihar Adamawa.

 

Advertisement

Lamarin ya faru ne bayan motar, makare da yashi ta kwace, ta yi cikin wani garejin gyaran motoci, inda ta yi ajalin mutanen.

 

Advertisement

La’eeb: Abin Da Dan Aljanin Gasar Kofin Duniya Na Qatar Ke Nufi

Wani ganau ya shaida wa Aminiya cewa, “Tifar da ke dauke da yashi a lokacin ta kwace ne sannan ta kade mutanen a garejin kanikawa.

Advertisement

 

“Direban tifar ya tsere, amma mutane sun kona motar.”

Advertisement

 

Shi ma wani ganau, Yakubu Ayuba, ya ce, wutar da fusatattun matasa suka banka wa motar ta yadu ta koma wasu shaguna da ke wurin da abin ya faru.

Advertisement

 

Yakubu Ayuba ya bayyana cewa hatsarin ya auku ne a unguwar Vinukilang da ke wajen garin Yola.

Advertisement

 

Jami’an Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) da ’yan kungiyar agaji ta Red Cross ne suka kwashe gawarwakin daga wajen.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending