Connect with us

News

2023: ’Yan Siyasa Ne Ke Murde Zabe Ba Mu Ba – INEC

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), ta ce babu ruwanta da murdiyar zabe amma ’yan siyasa ne ke aikata hakan.

Advertisement

 

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin Kwamishinar hukumar ta Jihar Ebonyi, Onyeka Ugochi, yayin ganawarta da manema labarai da kungiyoyi a jihar.

Advertisement

Uwa Ta Aurar Da ’Ya Ba Tare Da Sanin Mahaifinta Ba A Kano

 

Ta ce, “INEC ba ta murdiyar zabe, ’yan siyasa ne ke aikata haka.”

Advertisement

 

Onyeka ta ce babu wata kafa da hukumar za ta bari wadda za ta ba da damar murdiyar zabe a 2023.

Advertisement

 

Ta kara da cewa, murde zabe a wannan karo abu ne mai wahalar gaske saboda kyakkyawan shirin da hukumar ta yi wa manyan zabukan 2023.

Advertisement

 

A cewarta, hukumar za ta yi iya yinta wajen tabbatar da sahihin zabe, kuma ba za ta bari kowane irin matsin lamba daga ko’ina ya yi tasiri a kanta ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending