News
Dan Gwamnan Nasarawa Ya Riga Mu Gidan Gaskiya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya A. Sule, ya yi rashin dansa mai suna Hassan A. A Sule.
Sakataren Yada Labarai ga Gwamnan, Ibrahim Addra ne ya tabbatar da rasuwar tasa a sanarwar da ya fitar da safiyar Juma’a.
Zan share wa talaka hawaye kan batun sauya takardun kuɗi, in ji Kwankwaso
“A madadin iyalin Mai Girma Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi A. Sule, na sanar da rasuwar dansa, Hassan A.A Sule, wanda ya rasu ranar Alhamis, 26 ga Janairu, 2023,” in ji sanarwar.
Marigayi Hassan ya bar duniya yana da shekara 36.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa za a yi jana’izar marigayin a garin Gudi, cikin Karamar Hukumar Akwanga da misalin karfe 10:00 na safe a ranar Juma’a.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
