Connect with us

News

Zaben 2023: Tinubu Ya Yi Nasara A Ogun, Atiku A Matsayi Na Biyu

Published

on

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe zaben shugaban kasa a jihar Ogun, inda ta doke jam’iyyar PDP da sauran jam’iyyun siyasa.

 

Advertisement

A cewar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a jihar Ogun, dan takarar jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya zo na daya da kuri’u 341,554, yayin da Atiku Abubakar na PDP ya samu kuri’u 123,831.

 

Advertisement

A matsayi na uku, na hudu da na biyar, Peter Obi na Labour Party (LP) ya samu kuri’u 85,829, Dumebi Kachikwu na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) da 10,529, sai Rabiu Kwankwaso na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) 2,200.

Adadin masu kada kuri’a a jihar ya kai 2,687,606 inda jimillan wadanda aka amince da su ya kai 612,341.

Advertisement

 

Adadin kuri’un da aka kada ya kai 611,448, wanda ya kunshi sahihin kuri’u 580,124 da kuri’u 31,324 da aka ki amincewa.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Channel

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending