News
Jerin Sunayen Masu Mukamai 10 A Lokacin Buhari Da Ya Kamata Tinubu Yasa ayi Bincika akan su
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Tsohon mataimakin sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar APC na ƙasa Timi Frank, ya buƙaci shugaba Tinubu ya binciki wasu masu manyan mukamai a tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Timi Frank ya ce ya kamata Tinubu ya gudanar da bincike a kan zargin cin zarafin ofishin wasu daga cikin su, kuma kada a bari su guje wa hukunci.
Hukumar tsaro ta DSS ta bankaɗo barazanar kai hare-hare lokacin bukukuwan sallah
Fimi Frank ya bayyana sunayen ‘yan majalisar ministocin Buhari da ya kamata su kasance a komar Hukumomin EFCC da Kuma DSS.
Ya ce ya kamata a binciki Timipre Sylva, da Sanata Hadi Sirika da Abubakar Malami da Mele Kyari da Sadiya Umar Farouq da Hadiza Bala Usman Kanar Hammid Ali.
Sauran sun hada da – Babban jami’in Hukumar Kula da Tsaron Ruwa ta Nijeriya Bashir Jamo, da Tsofaffin manajojin daraktoci da shugabannin Hukumar Raya Yankin Neja-Delta NDDC da duk shugabannin tsaron da aka yi wa ritaya cikin kwanakin nan.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
