News
Hadarin mota yayi sanadiyar mutuwar mutane 31 a Adamawa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Adamawa ta ce mutane 31 ne suka mutu sakamakon hadurran mota daga watan Janairu zuwa Yuli na wannan shekara.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa mutane 274 ne suka samu raunuka daban-daban a hadarurrukan da aka yi a lokacin da ake tantance su.
Mista Yelwa Dio, Kwamandan hukumar FRSC a jihar, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dallancin labarai na kasa NAN a Yola ranar Asabar.A cewar Dio, a cikin wannan lokacin, rundunar ta yi rikodin hadarurruka 126 da suka hada da mutane 548.
Gwamnatin Sojin Jamhuriyyar Nijar Ta Musanta Korar Jakadan Najeriya
Ya alakanta manyan abubuwan da ke haddasa hadurran da wuce gona da iri, da yawan lodin mutane da kayayyaki, wuce gona da iri da kuma amfani da wayoyin hannu yayin tuki.
Don haka kwamandan sashin ya shawarci direbobi da sauran masu amfani da hanyar da su rika bin ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa don gujewa hadarin .
“Ya kamata direbobi su fahimci cewa fasinjoji na da ‘yancin isa inda suke cikin aminci.
“Haka zalika ya kamata fasinjoji su rika tattaunawa da direbobi kan bukatar bin ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa a kowane lokaci,” inji shi.
