News
Akwai Yiwuwar Ta Yanar Gizo Za A Yanke Hukuncin Zaben Gwamnan Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wata kwakkwarar majiyar tsaro ta shaida wa jaridar Aminiya a Kotun da za ta yanke hukunci kan zaben gwamnan Kano cewa har yanzu ba su san inda alkalan kotun suke ba, kuma da alamar ba za zo zaman da kansu ba.
Majiyar ta ce akwai yiwuwar alkalan za su halarci zaman ne ta bidiyo ta yanar gizo su kuma yanke hukunci, bisa umarnin da suka samu daga sama, saboda wasu dalilai na tsaro.
Ƴan sanda sun kori ƴan jarida daga kotu duk da sammakon da sukayi tun karfe 5 na Asuba.
Hakan na zuwa ne a yayin da ake yi ta tayar da jijiyar wuya a harabar kotun, bayan jami’an tsaro sun shaida wa bangarorin da ke shari’ar cewa mutum 50 kacal, ciki har da su da ‘yan jarida da lauyoyi kadai aka amince su shiga cikin kotun.
Jatidar Inda Ranka ta kawo rahoton yadda aka tsaurara matakan tsaro a harabar kotun da kewaye domin tabbatar da doka da oda.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
