Connect with us

News

Tsadar Rayuwa: Matsalolin mu ba daga Allah bane ba – Shehu Sani

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Tsohon dan majalisar dattawa na jihar Kaduna kuma mai sharhi kan al’umma, Sanata Shehu Sani, a ranar Litinin, ya ce matsalar tattalin arzikin da Najeriya ke fama da shi ba daga Allah ba ne ba.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, mai sharhin zamantakewar al’umma ya ce Najeriya na da albarkatun kasa da wasu kasashe ba za su taba samu ba.

Yadda Za Ka Siyi Data Akan Farashi Mai Rahusa —BAHAL DATA

Bayanin hakan na zuwa ne a daidai lokacin da wani rahoto da ke nuni da cewa dimbin jama’a sun kewaye ofishin hukumar kwastam ta shiyyar da ke Yaba a Legas, domin sayen buhunan shinkafa da aka yi wa rangwame mai nauyin kilogiram 25 da ake soka a kan farashi mai rahusa, lamarin da ya janyo turmutsitsin da aka yi hasarar wasu rayuka.

Sani ya bayyana cewa matsalar kasar nan ba ta Allah ba ce domin akwai koguna sama da 200 a kasar da ke da kyakkyawan filin noma mai fadin kilomita 923,768.

A cewarsa, Najeriya tana da mazaje da mata masu haihuwa fiye da kowace kasa a Afirka.

Advertisement

Ya rubuta cewa, “Akwai koguna sama da 200 a kasar nan kuma muna da kyakkyawar kasar noma mai girman kilomita 923,768. Muna da albarkatun kasa da wasu kasashe ba za su taba samu ba. Muna da maza maza da mata masu haihuwa fiye da kowace ƙasa a nahiyarmu.

“Ba mu da girgizar ƙasa, guguwa ko damina. Abin da zai iya girma a Thailand, Pakistan ko Brazil zai iya girma a wannan ƙasa.

 

DAILY POST 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending