News
DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Kano Ta Maka Tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, Matarsa, Hafsat Da Wasu Mutane 6 A Kotu Akan Zargin Cin Hanci Da Rashawa.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin jihar Kano ta maka tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa, Hafsat Umar, Umar Abdullahi Umar da wasu mutane biyar a gaban kotu, bisa zarge-zarge 8 da suka hada da cin hanci da rashawa da karkatar da wasu kudade da suka shafi biliyoyin naira.
Wannan yana kunshe ne a cikin takardar tuhuma mai kwanan wata 3 ga Afrilu, 2024 tare da lissafta jerin shaidu 15 masu gabatar da kara.
SOLACEBASE ta ruwaito cewa sauran wadanda ake kara a karar sun hada da Abdullahi Umar Ganduje, Hafsat Umar, Abubakar Bawuro, Umar Abdullahi Umar, Jibrilla Muhammad, Lamash Properties Ltd, Safari Textiles Ltd da Lesage General Enterprises.
Details soon
-
Opinion4 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion4 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Jihar Kano Ta Shiga Jerin Jahohi 10 Mafi Tara Kudaden Shiga Na VAT A 2026
