Connect with us

News

Hezbollah ta sanar da kai hari ga sojojin Isra’ila

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hezbollah a ranar Litinin ta bayyana cewa ta kai hari kan wani gini da sojojin Isra’ila ke amfani da shi a arewacin Isra’ila.

Advertisement

A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar ta ce ta kai hari kan wani gini da sojojin Isra’ila ke amfani da shi a matsugunin Margaliot da “makaman da suka dace,” inda suka ce sun samu “tabbataccen sakamako.”

Mutane 5 sun jikkata a rikicin manoma da makiyaya a Jigawa – ‘Yan sanda

Tashar talabijin ta Channel 12 ta Isra’ila ta bayar da rahoton faruwar lamarin a safiyar yau litinin, inda ta ce wani makami mai linzami da aka harba daga kasar Lebanon ya fada wani gini a garin Margaliot.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending