News
Gwamnatin Taraiya ta amince da kashe Naira Biliyan 2 domin sayen shanu a Taraba
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Ministar Jinƙai da Rage Raɗaɗin Ibtila’i da Ci gaban Al’umma ta Ƙasa, Sadiya Farouq ta baiyana cewa Majalisar Ƙoli ta ƙasa ta amince da fitar da kuɗi, wuri na gugar wuri har Naira Biliyan 2 domin sayen shanu don bunƙasa noman dabbobi a Jihar Taraba.
Da ta ke tattaunawa da manema labarai a fadar Shugaban Ƙasa a jiya Laraba, Ministar ta baiyana cewa tuni ma’aikatar ta ta aika da ƙunshin bayanan buƙatar ma’aikatar guda biyu.
Farouq ta ƙara da cewa ɗaya da ga ciki shi ne na neman sabunta kuɗin da za a kashe wajen sayo shanu a Taraba a karkashin Shirin Tallafin Gaggawa ga jihohin da su ka samu ibtila’in rigingimu da rashin tsaro.
Ministar ta ce ma’aikatar ta samu sahakewar kuɗaɗe da su ka kai naira biliyan biyu da ɗoriya.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News7 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
