News
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 179 A Najeriya —Hukumar NEMA
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar Agajin Gaggauwa ta Najeriya NEMA ta ce adadin mutanen da ambaliyar ruwa tayi sanadiyar mutuwar su a jahohi 15 na Najeriya ya kai 179, yayin da ambaaliyar ta shafi akalla mutane dubu 208,655 a jahohi 22.
A Alhamis ɗin nan ne dai Hukumar NEMA ta bayyana halin da ake ciki game da irin ta’adin da ambaliyar ruwa ta haifar a sassan Najeriya, inda ta ce akalla kadada dubu 107,652 ta shafe, ta kuma lalata gidaje dubu 80,049.
Cutar Mashako Tayi Sanadiyar Mutuwar Mutum 40 Bayan Sake Ɓulla A Kano
Daga cikin jahohin da iftila’in ya shafa akwai jihar Ribas da Neja da Benue da kuma jahohin da dama da ke ke yankin arewacin Najeriya.
Akalla ƙananan hukumomi 137 daga jahohi 28 ne ambaliyar ruwan bana ta shafa kamar yadda hukumar ta bayyana.
A ziyarar da kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Femi Gbajabiamila ya kai ofishin Hukumar NEMA, Darekta Janar na hukumar, Zubaida Umar, ta ce NEMA ta gudanar da bincike a kusan dukannin jahohin ƙasar dangane da iftila’in, sannan ta ƙara da cewa rashin samun tallafin kuɗi ne babbar matsalar da ke shafar aikin hukumar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
