Connect with us

News

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40  Sanadiyyar Hatsarin Kwale-kwale

Published

on

kwale kwale

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Gwamnatin Zamfara ta tabbatar da mutuwar mutane 40 bayan wani hatsarin kwale-kwale a ƙaramar hukumar Gummi da ke jihar.

Advertisement

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jirgin kwale-kwalen ɗauke da mutane sama da 40 a ranar Lahadin da ta gabata ya kife a kogin Bakin Kasuwa na unguwar Uban Dawaki.

Babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan harkokin yaɗa labarai da yada labarai Sulaiman Idris, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce gwamnan ya bayyana lamarin a matsayin wani babban iftila’i.

Advertisement

Ya kuma ƙara da cewa gwamnan ya umarci kwamishinan agaji da ya kai kayan tallafi cikin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa da iyalansu.

Idan dai za a iya tunawa, a baya-bayan nan ma dai wata ambaliyar ruwa ta lalata gidaje sama da 2000 da amfanin gona da dama da darajarsu ta kai miliyoyin Naira a ƙaramar hukumar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending