Connect with us

News

Likita Daya Na Kula Da MarasA Lafiya 33,000 A Kano — Ƙungiyar Likitoci

Published

on

Kungiyar Likitoci Za Su Shiga Yajin Aiki A Ranar Cikar Najeriya Shekara 64 Da Samun ’Yancin Kai

DAGA NUSIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

Kungiyar likitocin hakori ta kasa ta ce akwai kimanin mutum miliyan 20, amma likitoci 600 ne kawai suke duba su, wanda hakan ke nufin likita ɗaya na kula da marasa lafiya 33,000 a jihar Kano.

Advertisement

Haka zalika Likitocin sun bayyana damuwarsu kan rashin isassun likitocin da za su ke duba marasa lafiya, wanda hakan ya sa suke shirin tafiya yajin aiki daga ranar 1 ga watan Oktoba.

Kungiyar Likitoci Za Ta Shiga Yajin Aiki A Ranar Samun ’Yancin Kai

Ƙungiyar Likitocin ta bayyana hakan, yayin wani taron manema labarai da sakataren ƙungiyar, Dokta Anas Idris Hassan kamar yanda jaridar NIGERIAN TRACKER ta ruwaito

Advertisement

Ya ce gwamnatin jihar ta amince a watan Yuni za ta biya musu buƙatunsu, amma har yanzu ba ta ɗauki wani mataki ba.

Dokta Anas ya kuma bayyana cewa likitocin da aka ɗauka aiki a watan Satumban 2023 ba su samu albashinsu ba.

Advertisement

Likitocin sun kuma koka kan yanayin asibitocin Kano da rashin manyan kayan aiki.

Babbar matsalar ita ce ƙarancin likitocin da za su ke duba marasa lafiya.

Advertisement

Saboda waɗannan matsaloli, likitocin suka yanke shawarar tafiya yajin aiki daga ranar 1 ga watan Oktoba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending